Home
Categories
EXPLORE
True Crime
Comedy
Society & Culture
Business
Sports
Technology
Health & Fitness
About Us
Contact Us
Copyright
© 2024 PodJoint
Loading...
0:00 / 0:00
Podjoint Logo
US
Sign in

or

Don't have an account?
Sign up
Forgot password
https://is1-ssl.mzstatic.com/image/thumb/Podcasts221/v4/b6/6f/72/b66f7251-c078-a8f3-29b4-32bed8298330/mza_9500036076761979941.jpg/600x600bb.jpg
Najeriya a Yau
Muslim Muhammad Yusuf, Ummu Salmah Ibrahim
863 episodes
15 hours ago
Send us a text Halin matsin tattalin arziki ya tilasta da yawa daga cikin mutane zama a bacoci a garin Abuja da wasu biranen Najeriya. Mutane a birane kamar Abuja da Legas Da Fatakwal na cikin halin matsi sakamakon rashin ingattaccen muhalli. Ko wannen irin rayuwa irin wadannan mutanen ke yi? Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai a yau da ake bikin ranar muhalli ta duniya.
Show more...
News Commentary
News,
Politics
RSS
All content for Najeriya a Yau is the property of Muslim Muhammad Yusuf, Ummu Salmah Ibrahim and is served directly from their servers with no modification, redirects, or rehosting. The podcast is not affiliated with or endorsed by Podjoint in any way.
Send us a text Halin matsin tattalin arziki ya tilasta da yawa daga cikin mutane zama a bacoci a garin Abuja da wasu biranen Najeriya. Mutane a birane kamar Abuja da Legas Da Fatakwal na cikin halin matsi sakamakon rashin ingattaccen muhalli. Ko wannen irin rayuwa irin wadannan mutanen ke yi? Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai a yau da ake bikin ranar muhalli ta duniya.
Show more...
News Commentary
News,
Politics
Episodes (20/863)
Najeriya a Yau
Shekara Nawa Shugabanni Ke Bukata Don Cika Alkawarin Da Suka Dauka?
Send us a text Duk bayan shekaru hudu, Najeriya na kara yin zabe kuma ko wanne lokaci 'yan takara kan dauki alkawurika. Ko shekaru nawa wadanda ake zabe ke bukata don cika alkawuran da suka dauka? wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.
Show more...
15 hours ago
27 minutes

Najeriya a Yau
Mummunan Tasirin Rashin Bambance Zazzabin Lassa Kan Lafiyar Al’umma
Send us a text A cewar masana harkar kiwon lafiya, rashin tantancewa balle a bayar da kulawar da ta dace a kan lokaci na cikin dalilan ta’azzarar barazanar da Zazzabin Lassa ke yi ga bangarori da dama na rayuwar al’ummar Najeriya, musamman a yankunan karkara. Wani bincike a kan tasirin Zazzabin Lassa a kan rayuwar ‘’yan Najeriya wanda aka wallafa bara a mujallar Springer ya nuna gudunmawar da jahilci yake taimakawa wajen yaduwar cutar a kasar. A sassan Najeriya da dama dai, ba kasafai mutane...
Show more...
1 day ago
28 minutes

Najeriya a Yau
Yadda Ayyuka Suka Ragu A Jihohi Bayan Kudin Shiga Ya Karu
Send us a text Duk da karin kudin da gwamnatoci a matakin jiha suke samu daga asusun tarayya, ’yan Najeriya da dama suna korafin ba sa gani a kas. Manazarta dai sun ce ko kafin karin ma ya kamata ya yi a ce ayyukan da gwamnatcin jihohi suke yi sun fi da ake gani Ko mene ne ya sa jihohi “ba sa kashe karin kudaden da suke samu yadda ya kamata”? Wannan shi ne batun da shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.
Show more...
3 days ago
24 minutes

Najeriya a Yau
Yadda Talauci Ke Hana Shayar Da Yara Nonon Uwa Zalla A Najeriya
Send us a text Ga alama kwalliya ba ta biyan kudin sabulu a fafautukar da ake yi ta ganin iyaye mata sun shayar da jariransu nono Zalla a wata shida na farko. Rahotanni sun ce duk da dadewar da aka yi ana wayar da kai har yanzu matan da suke shayar da yara nono uwa Zalla ba su haura kashi 29 cikin dari ba. Shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan dalilan da suke hana mata shayar da ‘ya’yan su nono zalla na watanni shida.
Show more...
4 days ago
25 minutes

Najeriya a Yau
Me Dokar Kasa Ta Ce Kan Karin Wa’adin Aiki Da Shugaban Kasa Keyi?
Send us a text Bayan Karin wa’adin aiki da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu yayi ga kwanturola janar na hukumar hana fasa kwauri ta kasa Bashir Adewale Adeniyi ne dai lamarin ke ta shan suka daga mutane daban-daban. Yayin da wasu ke ganin abinda shugaban kasan yayi daidai ne, wasu kuwa na ganin hakan yayi hannun riga ga tanade-tanaden kundin tsarin mulkin kasa. Ko me dokar kasa tace game da wannan Karin wa’adi da shugaban kasan yayi? Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lo...
Show more...
1 week ago
22 minutes

Najeriya a Yau
Tinubu Ya Yi Adalci Ga Ayyuka Da Mukamai Tsakanin Kudu Da Arewa—Bayo Onanuga
Send us a text Kungiyar tuntuba ta Arewa ta zargi shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da kin yin daidaito wurin ayyuka da raba mukamai tsakanin Arewa da Kudancin Kasar nan. Wadannan zarge-zarge suka sa fadar Shugaban Kasa ta hannun mai taimaka masa na musamman kan kafofin yada labarai Bayo Onanuga maida martani ga Kungiyar ACF. Ko wadanne irin martani fadar shugaban kasar ta mayar ga kungiyar Tuntuba Ta Arewa? Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.
Show more...
1 week ago
27 minutes

Najeriya a Yau
Yadda Za A Dama Da Matan Arewa A Fannin Kimiyya
Send us a text Mata a Arewacin Najeriya na fuskantar kalubale da dama a fannin karantar kimiyya Akwai darussan da a mafi yawan lokuta ba mata kadai ba, har da mazan na kaurace musu. Shirin Najeriya a Yau ya yi nazari ne kan dalilan da suka sa matan Arewacin Najeriya ke tsoron karantar ilimin kimiyya.
Show more...
1 week ago
30 minutes

Najeriya a Yau
Matakan Karfafa Gwiwar 'Yan Najeriya Kan Zabe—INEC
Send us a text ‘Yan Najeriya da dama ne dai aka bayyana basa fitowa kada kuri’a a duk lokacin da zabe ya zagayo. Wasu daga cikin ‘yan Najeriya sun bayyana dalilan su da suka hada da rashin jin dadin abun da hukumar zabe keyi, rashin yadda da sakamakon zabannin da suka gabata da dai sauran su a matsayin dalilan su. Ko wadanne matakai hukumar zabe INEC take dauka don karfafawa ‘yan Najeriya gwiwan fitowa kada kuri’a a 2027? Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi n...
Show more...
1 week ago
19 minutes

Najeriya a Yau
Yadda Masu Yi Wa Kasa Hidima Za Su Ci Arzikin Yankunan Da Suke AIki
Send us a text Bayan hadin kai da karfafa fahimtar juna wadanda hidimar kasa take kawowa, akan samu wasu masu hidimar da sukan yi amfani da duk wata dama da suka samu don neman na sakawa a bakin salati. Yayin da wasu masu hidimar kasa sukan kama sana’a ko su saka hannun jari a inda aka tura su, wasu kuwa komawa garuruwansu suke yi bayan sun kammala. Shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne a kan irin damar da masu yi wa kasa hidima suke da ita a garuruwan da aka tura su.
Show more...
2 weeks ago
22 minutes

Najeriya a Yau
Cutukan Da Rumar Daki Ke Haifarwa Ga Jikin Mutum
Send us a text Malaman kiwon lafiya sun bayyana yadda ruma ke yada matsalolin rashin lafiya ga lafiyar jikin mutum. Musamman a lokuta irin na ruwa, ruma kan dabaibaye gidajen mutane da dama na tsawon lokaci wanda ka iya jawo matsaloli daban daban ga lafiya da kuma gidajen mu. Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan irin matsalolin da ruma ke haifarwa ga lafiyar jikin mu.
Show more...
2 weeks ago
22 minutes

Najeriya a Yau
Yadda Farashin Taki Ke Hana Noman Masara Da Shinkafa
Send us a text Tashin farashin takin zamani yana hana manoma da dama noman wasu nau’ukan abinci. Manoma da dama dai suna kauracewa shukan masara da shinkafa da aka fi amfani da su a Najeriya sakamakon tsadar takin zamani, inda masana suke ganin in ba’a dauki mataki ba hakan zai kawo karancin abinci a Najeriya. Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan dalilan da suka sa farashin takin zamani yayi tashin gwauron zabi a Najeriya.
Show more...
2 weeks ago
25 minutes

Najeriya a Yau
Abin da ya sa muke yi wa PDP zagon ƙasa — Sule Lamiɗo
Send us a text Zagon kasa da wasu ‘ya’yan PDP ke yi mata na kara ta’azzara, inda wasu ke zama a cikin ta amma suke wa jam’iyyun adawa aiki. Ko a kwanan nan, an hangi wasu daga cikin ‘ya’yan jam’iyyar a taron hadakar ADC, wadda hakan ke jaddada har yanzu PDP ta kasa kawo karshen wannan matsala. Ko me yasa ‘ya’yan PDP ke yiwa jam’iyyun adawa aiki? Wannan ne batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.
Show more...
2 weeks ago
26 minutes

Najeriya a Yau
Shin Ya Kamata A Samar Da Dokokin Da Za Su Sa Ido Kan Amfani Da AI?
Send us a text Tun bayan bayyanar kirkirarrriyar basira wato AI ne dai wasu mutane suke amfani da ita ta hanyar da da bai kamata ba. Wasu sukan yi amfani da ita wajen saka hoto ko kirkirar faifan bidiyo wanda zai nuna wani yana yin abun da bai kamata ba. Hakan dai ya sa wasu suna ganin ya kamata a samar da dokokin da za su rinka lura da yadda ake amfani da kirkirarriyar basirar. Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne a kan dacewar sanya doka gane da yadda mutane za su rinka...
Show more...
3 weeks ago
22 minutes

Najeriya a Yau
Dalilan Da Suka Sa 'Yan Najeriya Ba Sa Samun Adalci
Send us a text Rashin samun adalci a Najeriya ba ya rasa nasaba da cin hanci da rashawa a bangaren shari’a, inda ake zargin wasu jami’ai suna karɓar kuɗi kafin su yanke hukunci, kamar yadda manazarta suka bayyana. Ko mece ce gaskiyar wannan lamari? Wannan ne batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.
Show more...
3 weeks ago
19 minutes

Najeriya a Yau
Wa Zai Gaji Buhari A Fagen Siyasar Najeriya?
Send us a text Gaskiya da rikon amana suna cikin dalilan da suka sa tsoon Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi fice a siyasar Arewacin Najeriay. Wasu masana da ma makusantar tsohon Shugaban kasar dai suna ganin Arewa ta yi rashi kuma zai yi wuya a samu makwafansa. Yayin da ake binne marigayin, hankalin wasu 'yan Najeriya ya fara komawa ga yiwuwar samun wanda zai iya maye gurbinsa a fagen siyasar Najeriya. wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari...
Show more...
3 weeks ago
24 minutes

Najeriya a Yau
Abin Koyi Daga Rayuwar Marigayi Muhammadu Buhari-- Makusantansa
Send us a text Rasuwar tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ta sa 'yan Najeriya da dama kaduwa duk da cewa ya jima yana fama da rashin lafiya. Sanar da rasuwar ke da wuya, 'yan kasa suka fara bayyana ra'ayoyi daban daban akan abin da suka gani game da rayuwar tsohon shugaban. Amma makusantansa sun bayyana wasu halaye game da shi wadanda ba kowa ne ya sani ba. Sune kuma shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.
Show more...
3 weeks ago
24 minutes

Najeriya a Yau
Dalilan Da Wasu Matasa Ba Sa Aiki Tukuru Wajen Neman Arziki
Send us a text Matasan Najeriya da dama suna son yin arziki amma ba tare da sun sha wahala ba. Sau da yawa matasa sun fi neman hanya mafi sauki da za ta basu arziki ba tare da sun sha wahala ba. Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan dalilan da suka sa wasu matasa bin yanke don tara abin duniya.
Show more...
4 weeks ago
24 minutes

Najeriya a Yau
Abin Da Ya Sa ’Yan Najeriya Ba Sa Cin Kifi Yadda Ya Kamata
Send us a text Duk da amfanin kifi ga lafiyar jikin mutum da kuma samar da kudin shiga masana sun ce ba a amfani da shi yadda ya kamata a Najeriya. Baya ga bai wa jiki lafiya, kifi ka iya samar da kudaden shiga ga daidaikun ’yan Najeriya da ma kasar gaba daya. Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan dalilan da suka sa ’yan Najeriya basa samun cin kifi kamar yadda ya kamata.
Show more...
4 weeks ago
27 minutes

Najeriya a Yau
Sarkakiyar Dake Gaban Hadakar ADC -- Atiku Ko Peter Obi?
Send us a text 'Yan Najeriya suna ci gaba da tafka muhawara a kan wanda jamiyyar hadaka ta ADC zata tsayar takarar Shugaban Kasa a zaben 2027. Yayin da wasu suke ganin Atiku Abubakar yana da dimbin magoya baya, wasu kuwa gani suke yi shi ma Peter Obi ba kanwar lasa bane. Ko me zai faru idan daya daga cikin su ya samu tikitin tsayawa takara a 2027? Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne a kan wannan lamari.
Show more...
1 month ago
26 minutes

Najeriya a Yau
Mene Ne Tasirin Nadin Mataimaka Na Musamman A Rayuwar Jama’a?
Send us a text Wadanda aka zaba su rike mukaman gwamnati kan nada wasu mukarrabai don su taya su sauke nauyin da aka dora musu. Wasu na zargin nadin baya rasa nasaba da sakayya ga irin rawar ga wadanda aka nada saboda rawar da suka taka yayin yakin neman zabe. Ko irin wadannan nade-nade na da wani tasiri ga rayuwar alumma? Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan nade-naden masu taimakawa shugabanni da irin tasirin da suke dashi.
Show more...
1 month ago
25 minutes

Najeriya a Yau
Send us a text Halin matsin tattalin arziki ya tilasta da yawa daga cikin mutane zama a bacoci a garin Abuja da wasu biranen Najeriya. Mutane a birane kamar Abuja da Legas Da Fatakwal na cikin halin matsi sakamakon rashin ingattaccen muhalli. Ko wannen irin rayuwa irin wadannan mutanen ke yi? Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai a yau da ake bikin ranar muhalli ta duniya.